FIFA za ta jagoranci koyar da ƙwallon ƙafa a makarantun Nijar
MAR 2, 2026-1 MIN
FIFA za ta jagoranci koyar da ƙwallon ƙafa a makarantun Nijar
MAR 2, 2026-1 MIN
Description
Shirin “Duniyar Wasanni” tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zai yi duba ne kan yadda aka sanya tsarin koyar da wasan kwallon ƙafa a makarantun Boko na Jamhuriyar Nijar. A wannan makon mun yi dubi ne kan shirin koyar da wasan kwallon ƙafa da za a sirka a tsarin koyarwa a makarantun Boko a Jamhuriyar Nijar, a ƙoƙarin da ake yi na haɓɓaka harkar, ganin yanda take a baya sosai a jadawalin ƙasashe da hukumar kwallon ƙafa ta duniya FIFA ta fitar inda Nijar ɗin ta ke a mataki na 111. Shi dai wannan tsarin, ya kasance wani shiri ne na haɗin gwiwa da aka yi tsakanin hukumar FIFA da kuma gwamnatin Nijar wanda hukumar kwallon kafa ta ƙasar fenifoot ke kula da shi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.